Bisimillahir rahmanur rahim da sunan Allah mai rahama mai jin kai.        


     Sahabban manzon Allah (S.A.W) wadansu bayin Allah (S.W.T) da ya fifita su a cikin wannan al'ummar babu wani musulmi da zai ta ba kamo kafar sahabi ko ya hada kafa dashi a cikin daraja, ko mai kokarinsa a cikin wannan addinin matukar da shi ba sahabi ba ne, haka zalika kuma shima sahabi ba zai taba kamar kafar annabi Muhammad (S.A.W) ba bare ma ya hada kafa dashi a wajan daraja.

    
   Sai dai hakika Ubangiji madaukaki ya fifita darajojjin wadansu sahabban a kan  'yan uwansu sahabbai, kamar yadda ya fifita wasu annabawan akan 'yan uwansu annabawa tsira da amincin Allah su tabbata a gare su baki daya.


Mafi darajar Sahabbai a wajen ahlussunna da jama'a sune 

• Abubakar 

• Umar

 Allah yakara yadda a gare su. Amma kuma an samu sabani akan 

• Aliyu
• Usmanu
 
Allah yakara yadda a gare su baki daya. Wadansu sun fifita ALIYU akan USMANU, wadansu kuma sun fifita USMANU akan ALIYU. Amma kuma Imamu Malik ya ta ce, yace "ba za a fifita da a tsakanin USMANU da ALIYU ba" Allah yakara yadda a gare su. Amma yawanci malamai sun gabata da USMANU akan ALIYU (R.T.A).

    
    
      Abu Mansuru Albagdadiyi yace "abokanmu su hudu akan cewa Khalifofin Manzon Allah (S.A.W) sune mafiya daraja a cikin sahabbansa (S.A.W) Sannan sai mutane shida cikwan mutane goman da aka yiwa bushara sa aljanna. Wannan sahabbai guda shida sune 

Dalhat
Zubair
Sa'adu 
Sa'idu 
Abdurrahman 
Ubaidata

      Wadannan sune Sahabbai guda shida, idan ka hada da Khalifofinsa guda hudu sun zama guda goma kenan waddan da Allah yayi musu bushara da Aljanna a kan harshen Manzon Allah (S.A.W).

Post a Comment

Previous Post Next Post